Yadda za ku nemi aikin gwamnatin da za a ɗauki mutum 774,000 a Najeriya



Gwamnatin Najeriya ta kaddamar da shirin ayyuka na musamman, wanda za a dauki 'yan Najeriyar da ba su da aikin yi kimanin 774,000, wanda aka ƙaddamar a ranar Talata 5 ga watan Janairun shekarar 2021.

Hukumomin sun bayyana cewa wannan shiri zai dauki 'yan Najeriya 1,000 aiki daga ko wace karamar hukuma 774 a fadin kasar, wanda zai taimaka wajen rage matsalolin rashin kudin da annobar cutar korona ta haifar.

Hukumar samar da ayyukan yi ta kasar ce (NDE) za ta dauki nauyin shirin da kuma aiwatar da shi.

A wata hira da BBC, minista a Ma'aikatar Kwadago ta kasar, Mista Festus Keyamo, ya bayyana cewa domin tabbatar da an aiwatar da shirin cikin nasara, gwamnati ta shigar da shugabannin al'umma da na addinai biyu, da na kungiyoyi masu zaman kansu, da na kungiyoyin direbobi, har da na kungiyoyin mata 'yan kasuwa daga jihohi 36 na ƙasar cikin shirin.

''Wadannan shugabannin addinai su ne za su kafa kwamitoci a yankunansu, wanda zai duba yadda za su tantance wadanda za su ci gajiyar wannan shiri, saboda su suka fi kusa da irin talakawan da wannan shiri ke nufin taimaka wa,'' in ji ministan.

Gwamnatin Najeriyar ta ce, wannan shiri na wadanda ba su yi karatu bane ko kuma ba su da shaidar karatu inda za a dauke su aiki na tsawon watanni uku, kuma za a rika biyan su naira dubu ashirin (N20,000) a ko wane wata.

0/Post a Comment/Comments

Previous Post Next Post

header

Sponsor