IRIN MIJI DA KOWACCE MACE TAKESO MARSAYIN MIJIN AURE
Kamar yadda ba kowacce Mace Namiji ke so ba haka zalika ba kowana Namiji Mace ke so ba.
Akwai wasu siffofin nagari dake tattare da Mijin da kowacce macce ke so:
1-Mijin dake son matarsa bayan aurensu fiyeda yadda yake sonta a layi.
2-Miji mai kishin matarsa.Domin Annabi Sallallahu alaihi wasallam yace: (Duk wanda baya kishin matarsa bazai shiga Aljannah ba).
3-Mijin da ya dauki aure a matsayin Ibadah,ba wai abin wasa ba ko kuma abin jin dadin rayuwa kawai ba.
4-Wanda ya dauki matarsa a matsayin abokiyarsa, kanwarsa,almajirarsa,kuma abokiyar shawararsa.
5-Shine wanda baya zagin matarsa,baya cin mutuncinta,baya cin zalinta,baya ha’intarta koda a bayan idonta ne.
KARANTA:
- MAGANIN KAIKAYIN NONO
- DAREN FARKO AMARYA DA ANGO
- ILLOLIN SHAN FARJIN MACE KO TSOSAN AZZAKARIN NAMIJI
- ILLOLIN CUTAR KANJAMAU (HIV AIDS)
- ALAMOMIN CIWON ULCER
- ALAMOMIN CIWON SANYI
- MAGANIN SANYI
- MAGANIN DADEWA ANA JIMA'I DA MACE
- MAGANIN KARIN GIRMAN KUGU DA DUWAWU
- MAGANIN KARIN NI'IMA GA MATA
- MAGANIN MASTI NA MATA, YADDA ZAKI TSUKE GABANKI
- SHAWARWARI GA YAN MATA DA MATAN AURE
- HANYOYIN BIYAWA MIJINKI BUKATA YAYIN JININ AL'ADA (PERIOD
- YADDA AKE KULA DA JARIRIN YARO
- ABUBUWAN DA YAKAMATA MACE TA KIYAYE LOKACIN AL'ADA
- ABINCIN DA YAKE KARAWA NAMIJI DA MACE SHA'WA DA KUZARI YAYIN JIMA'I
- MATSALAR SAURIN INZALI DA YADDA ZA'A MAGANCETA
- YADDA AKE KWANCIYAR JIMA'I
- MAGANIN GIRMA DA TSAYIN AZZAKARI
- YADDA ZAKI GAMSAR DA MIJINKI A LOKACIN JIMA'I
- YADDA AKE MINING A REMITANO (RENEC COIN)
- ABUBUWAN DA NAMIJI YAKAMATA YASANI GAME DA MACE AKAN SOYAYYA
- YADDA CIKI YAKE SHIGA MACE DA YADDA AKE KULA DASHI HAR ZUWA HAIHUWA
- ALAMOMIN SOYAYYAR GASKIYA DAGA YA MACE
- MAGANIN KARA GIRMAN KUTURI/KUGU (HIPS)
6-Shine wanda yake zaune da iyalinsa cikin amana da gaskiya da kyautatawa ba cuta ba cutarwa.Wanda idan ya fahimci halayen matarsa, yake hakurin zama da ita tare da kyautatawa domin neman rahamar Allah Ta’ala.
7-Shine wanda idan zai yi magana da matarsa, zai fadi gaskiya babu yaudara ko karya acikin zancensa.
8-Shine wanda ya dauka a zuciyarsa cewa: Iyayen matarsa,Iyayensa ne. ‘Yan uwanta ma‘yan uwansa ne,kuma dangin matarsa danginsa ne
9-Shine wanda yake daukar cewa farin cikin matarsa shine farin cikinsa kuma matsalar ta,itama tasa ce.
10-Shine wanda ke kokarin kiyaye sirrin matarsa,kuma yake kokarin kare mata mutuncinta koda a wajen ‘yan uwansa ne, tare da hikima da fahimtarwa.
11-Shine wanda baya fifita matarsa akan ‘yan uwansa,kuma baya tauye mata darajarta.Yana bawa kowanne gefe nasa hakkin kamar yadda shari’ah ta tanadar.
12-Shine wanda ya tanadi ruwan afuwa da hakuri a cikin zuciyarsa domin kashe wutar tashin hankali da bacin rai a duk lokacin da hakan ta faru tsakaninsa da matarsa.
13-Shine wanda a kullum yake kokarin tarbiyyantar da iyalinsa akan rayuwar addinin Islama ba rayuwa irin ta yahudu da nasara ba.
14-Shine wanda yake zaune da matarsa komai dadi komai wuya ba zai dena nuna mata soyayya ba wai don tafara yankwanewa ko kuma karfinta yafara raguwa.
15-Shine wanda yake bawa matarsa yabo a duk lokacin da tayi kwalliya ko kuma tayi girki komai rashin dadinshi.Miji nagari baya raki baya ihu don yaji abinci yayi yaji ko gishiri yayi yawa. Sai dai yace: “uwargida abincin nan yayi dadi iyaka, sai dai gishiri yayi mana shisshigi a ciki”
Allah Yasa mazaje su gane,su sauke hakkinsu na Aure,
Allah shine mafi sani.
Post a Comment